Bakonmu A Yau

  • Author: Vários
  • Narrator: Vários
  • Publisher: Podcast
  • Duration: 1:32:09
  • More information

Informações:

Synopsis

A kullum mukan gayyaci masana a fannoni daban daban domin tattauna wasu muhimman al'amurra da suka shafi kanun labarai a duniya. wani lokacin kuma wasu manyan jami'an gwamnati da masu fada aji sukan kawo muna ziyara domin tattauna batutuwan da suka shafi matsalolin da suka shafe su ko kuma ci gaban kasa.

Episodes

  • Abdullahi Jalo akan ƙorafin arewa a game da jarabawar JAMB

    19/05/2025 Duration: 03min

    Da aalam dai har yanzu da sauran rina a kaba ga hukkumar JAMB, mai shirya jarabawar shiga manyan makarantu a Najeriya a game da matsalar da aka samu a lokacin jarabawar wannan shekarar sakamakon ƙorafin da wasu jihohin arewacin ƙasar ke yi akan ware wasu jihohi huɗu na kudu da hukumar ta yi don sake zana jarawabar. Tuni dai wasu suka yi barazanar zuwa kotu tare da kira ga gwamnati da ta saka baki a lamarin. Kan haka ne Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Barrister Abdullahi Jalo, masanin doka.

  • Farfesa Sheriff Almuhajir kan makomar yankin Tafkin Chadi a ɓangaren tsaro

    16/05/2025 Duration: 03min

    Babban Hafsan tsaron Najeriya, Laftanar Janar Christopher Musa ya ce baya ga amfani da makamai wajen tinkarar mayakan Boko Haram, farfado da Tafkin Chadi zai taimaka wajen samarwa jama'ar yankin sana'oi. Wannan ya biyo bayan ziyarar aikin da ya kai Maiduguri bayan kazaman hare haren da boko haram ta kai cibiyoyin soji.Dangane da wannan bukatar, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da wani mutumin yankin, Farfesa Sheriff Muhammad Almuhajir.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

  • Umar Saleh Gwani kan faɗuwar jarabawar JAMB a Najeriya

    15/05/2025 Duration: 03min

    Hukumar kula da jarabawar shiga manyan makarantu a Najeriya ta JAMB ta nemi gafarar jama'ar kasar saboda matsalolin da aka samu wajen jarabaswar bana, wadda ta kai ga dalibai sama da miliyan guda da rabi suka kasa samun makin da ake bukata. Shugaban hukumar Farfesa Ishaq Oloyede cikin hawaye ya nemi gafarar jama'a da kuma daukar alhakin lamarin.Dangane da wannan matsala, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Malam Umar Saleh Gwani masanin harkar sadarwa.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

  • Farfesa Khalifa Dikwa kan karuwar hare-haren Boko Haram a Borno

    14/05/2025 Duration: 03min

    Yayinda hare-haren ƙungiyar Boko Haram tsagin ISWAP ke ƙara tsananta musamman a Najeriya, rahotanni na cewa mayakan sun shafe ƙarshen makon jiya zuwa Litinin  da ta gabata suna kadammar da hare-hare a sassa na jihar Borno da ke arewa maso gabashin ƙasar.A tattaunawarsa da Rukayya Abba Kabara, Farfesa Khalifa Dikwa masanin tsaro a Najeriya ya ce ba abin mamaki bane yadda ‘yan ta’addar suka sauya salon kai hare-harensu. Shiga alamar sauti domin sauraron cikaken bayani.....

page 2 from 2