Dandalin Siyasa

Kun san abin da Buhari ya fada a Akwa Ibom?

Informações:

Synopsis

Shugaban Najeriya Muhammdu Buhari da ya kaddamar da yakin neman zabensa a jihar Akwa Ibom, ya bayyana nasarorin da ya samu tun bayan darewarsa kan karagar mulki a shekarar 2015, in da yake cewa, gwamnatinsa ta murkushe mayakan Boko Haram duk da cewa kungiyar kan kaddamar da hare-hare jifa-jifa a yankin arewa maso gabashin kasar. Shugaban ya kuma bayyana irin nasarar da ya samu a fannin yaki da cin hanci da rashawa. Kuna iya latsa kan hoton don sauraren cikakken shirin kan yakin neman zaben Buhari a Akwa Ibom.